Ku duniya ta ke yayi, dole mu hada kai wajen yada manufofin gwamnatin Kano – Waiya ga yan jaridun yanar gizo

Date:

 

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada kudirinta na hada kai da kafafen yada labarai na yanar gizo domin yada kudirori da manufofinta don sanar da duniya aiyukan da take yiwa al’umma .

” A wannan zamani ku duniya take yayi, domin suke abu zai faru yanzu-yanzu ku yada shi ga al’umma, amma sai dai akwai bukatar mu hada kai da ku wajen yakar masu yada labaran karya domin wannan al’amarin yana damun al’umma”. Inji Waiya

Sabon Kwamishinan Yada Labarai na Jihar, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya ne ya bayyana hakan a wata ganawa da yi da Kungiyar Mawallafa Jaridun Yanar Gizo (Association of Online Media Guild ASSOMEG) a fishinsa.

Talla

” Dani ni abokin yan jaridu ne yanzu kuma gwamnan Yusuf ya bani wannan mukamin don haka dole mu hada hannu waje guda da ku domin yada manufofin gwamnatin Kano, don haka Ina neman hadin kan ku, kuma Ina baku tabbacin za mu yi aiki tare”. A cewar Kwamishina Waiya

Kwamishinan ya jaddada bukatar yin tsari da hadin gwiwa da kafafen yada labarai na yanar gizo don tabbatar da yada sahihin ayyuka da manufofin gwamnati.

Gwamnati ta aiwatar da ayyuka da yawa, kuma suna bukatar a yada su. ” in ji shi.

A karon farko bayan cire shi daga sakataren gwamnatin Kano Baffa Bichi ya Magantu

Kwamishinan ya kuma yi kira da a hada kai a tsakanin ‘yan jarida na yanar gizo a Kano tare da bayyana shirin horas da dukkanin jami’an yada labarai da jami’an hulda da jama’a na jihar kan tsarin yada Labarai na zamani.

A nasa bangaren, Shugaban Kungiyar Mawallafa Jaridun Yanar Gizo ta The Association of Online Media Guild ASSOMEG Abdullateef Abubakar Jos, ya bayyana goyon bayansa ga yadda Kwamishinan ya ke mu’amalantar kafafen yada labarai.

“Mambobinmu kwararru ne, mun zo nan don taya ka murna, kuma muna goyon bayan matakin da ka dauka na kokarin hiras da ma’aikatanka wanda hakan zai taima wajen inganta harkokin yada labarai a Kano.” inji shi.

Abubakar Jos ya jaddada bukatar duba lamarin labaran bogi da kuma magance matsalar, wanda ya ce tana yin illa mai yawa ga kowacce gwamnati.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...