Dalilin da yasa za a fuskanci katsewar wutar lantarki na akalla sati biyu a Abuja

Date:

Kamfanin rarraba hasken wutar lantarki reshen babban birnin tarayya Abuja, ya ce wasu sassan birnin za su fuskanci katsewar lantarki na aƙalla makonni biyu.

Kamfanin na AEDC ya sanar da haka ne rana Juma’a a shafinta na X, inda ta ce za a fara fuskantar rashin wutar daga ranar Litinin da ke tafe.

Ta ce hakan zai faru ne sakamakon gyara da kuma komawa zuwa babban layin ba da wuta na megawatt 33 da kuma layin da ke bayar da wuta na megawatt 132 da ke Kukwaba.

A cewar kamfanin, za a yi aikin komawa babban layin ne daga ranar Litinin 6 ga watan Janairu zuwa 31 ga watan.

“Anguwannin da ɗaukewar lantarkin zai shafa sun haɗa da Lugbe da Airport Road da Kapwa da NNPC da Games Village da kuma National Stadium,” in ji sanarwar da kamfanin ya fitar.

Hukumar Tace Fina-fina ta Kano ta Dakatar da Babbar Jaruma a Kannywood

Ya ce sauran sun haɗa da Gudu da Gbazango da sassan Kubwa da Bwari da Jahi da sassan Jabi da Karu da Nyanya da Mararaba da kuma Keffi.

Ya ce sauran sun haɗa da Gudu da Gbazango da sassan Kubwa da Bwari da Jahi da sassan Jabi da Karu da Nyanya da Mararaba da kuma Keffi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...