Dalilin da yasa za a fuskanci katsewar wutar lantarki na akalla sati biyu a Abuja

Date:

Kamfanin rarraba hasken wutar lantarki reshen babban birnin tarayya Abuja, ya ce wasu sassan birnin za su fuskanci katsewar lantarki na aƙalla makonni biyu.

Kamfanin na AEDC ya sanar da haka ne rana Juma’a a shafinta na X, inda ta ce za a fara fuskantar rashin wutar daga ranar Litinin da ke tafe.

Ta ce hakan zai faru ne sakamakon gyara da kuma komawa zuwa babban layin ba da wuta na megawatt 33 da kuma layin da ke bayar da wuta na megawatt 132 da ke Kukwaba.

A cewar kamfanin, za a yi aikin komawa babban layin ne daga ranar Litinin 6 ga watan Janairu zuwa 31 ga watan.

“Anguwannin da ɗaukewar lantarkin zai shafa sun haɗa da Lugbe da Airport Road da Kapwa da NNPC da Games Village da kuma National Stadium,” in ji sanarwar da kamfanin ya fitar.

Hukumar Tace Fina-fina ta Kano ta Dakatar da Babbar Jaruma a Kannywood

Ya ce sauran sun haɗa da Gudu da Gbazango da sassan Kubwa da Bwari da Jahi da sassan Jabi da Karu da Nyanya da Mararaba da kuma Keffi.

Ya ce sauran sun haɗa da Gudu da Gbazango da sassan Kubwa da Bwari da Jahi da sassan Jabi da Karu da Nyanya da Mararaba da kuma Keffi

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

An Dauke Shaikh Abduljabbar Daga Gidan Yari na Kurmawa Zuwa Wani Wuri – Yan uwansaba

Wani labari da ke yawo a kafafen sada zumunta...

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...