Kungiyar DHS International ta yi Aikin Dubawa da Rabawa Marasa Lafiya Magani Kyauta a Kano

Date:

Daga Abubakar Lawan Bichi

Mataimakin Shugaban Kasa Senator Kashim Shettima GCON ya kaddamar da duba marasa lafiya tare basu magunguna kyauta da bada taimako abinci ga Jama’a a Kwaleji Ilimi ta Tarrayya dake Bichi wanda ya dauki nauyi ta Kungiyar DHS International & Project Rescue Nigeria wanda ya gudana a Babban dakin taro na Kwalejin.

Mataimakin Shugaban Kasa Wanda Sanata Abba Aji ya wakilta, ya ce gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tunibu zata cigaba da ingarta rayuwa Jama’a.

Sanata Abba Aji ya kira da masu hannu da shuni dasu taimaka Jama’a.

Talla

A jawabinsa Shugaban Kungiyar DHS International & Project Rescue Nigeria team na Kasa Amb. Dr Ibrahim Bala Aboki ya ce a matsayisa na Shugaban Kungiyar sun zabi a fara gabatar da shirin a garin Bichi a matsayinsa na tsohon dalibi na Kwalejin ta Bichi duba da irin gudumarwa da aka basu a rayuwa yayi da suke karatu a Kwaleji.

Yace sun zabi Cututtukan da suka fi damun Jama’a Kamar Olcer, ciwon suga, zabarbin cizon sauro da sauransu domin ba da ganinsu.

Ya kara da cewa Kungiyar zata cigaba da bada wannan tallafi karkashin Jagoranci uban kungiyar na Kasa Mataimakin Shugaban Kasa Senator Kashim Shettima GCON.

Shi ma a nashi Jawabin Shugaban Kwaleji ta FCE Bichi Dr Bashir Sabo Abubakar ya godewa Mataimakin Shugaban Kasa Senator Kashim Shettima GCON tare da Kungiyar DHS International bisa bada wannan tallafi ga Jama’a sama da dari biyar 500.

Taro ya sami halatar Dan uwar ga Mataimakin Shugaban Alh Usman Shettima, Mallam Musa Aliyu Jahun (Magajin Mallam), Alh Yakubu Ibrahim tagaho (Sarkin noman Gaya), Alh Ibrahim Haruna BBY, Alh Audu Ladiyo da Kuma Alh Danladi Wadari da sauran Jama’a da dama.

Ga hotunan yadda taron ya Kasance

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...