Kotu ta ki bayar da belin Yahya Bello

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ki bayar da belin Yahya Bello.

Tsohon gwamnan na jihar Kogi ya bayyana a gaban kotun yau Talata, domin neman beli kan shari’ar da ake yi masa.

Ana zargin Yahya da halasta kuɗin haram da suka haura naira biliyan 100 wanda ya karkata lokacin yana gwamna, a cewar hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC.

Talla

Da take yanke hukunci, mai shari’a Maryanne Anenih, ta ce an gurfanar da Bello ranar 27 ga watan Nuwamba, bayan da jami’ai suka kama shi ranar 26 ga watan. Sai dai an buƙaci belinsa ranar 22 ga watan na Nuwamba, kwanaki da dama kafin ma ya gurfana.

Yan sanda a Kano sun bayyana adadin mutanen da suka rasu a fadan daba

Mai shari’ar ta ce ya kamata a bukaci beli ne bayan an gurfanar da wanda ake ƙara.

“Buƙatar beli da Yahya ya yi tun da farko ba ya kan tsari, don haka ne muka yi watsi da shi,” in ji mai shari’a Maryanne Anenih.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...