Kotu ta ki bayar da belin Yahya Bello

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta ki bayar da belin Yahya Bello.

Tsohon gwamnan na jihar Kogi ya bayyana a gaban kotun yau Talata, domin neman beli kan shari’ar da ake yi masa.

Ana zargin Yahya da halasta kuɗin haram da suka haura naira biliyan 100 wanda ya karkata lokacin yana gwamna, a cewar hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC.

Talla

Da take yanke hukunci, mai shari’a Maryanne Anenih, ta ce an gurfanar da Bello ranar 27 ga watan Nuwamba, bayan da jami’ai suka kama shi ranar 26 ga watan. Sai dai an buƙaci belinsa ranar 22 ga watan na Nuwamba, kwanaki da dama kafin ma ya gurfana.

Yan sanda a Kano sun bayyana adadin mutanen da suka rasu a fadan daba

Mai shari’ar ta ce ya kamata a bukaci beli ne bayan an gurfanar da wanda ake ƙara.

“Buƙatar beli da Yahya ya yi tun da farko ba ya kan tsari, don haka ne muka yi watsi da shi,” in ji mai shari’a Maryanne Anenih.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...