Kotu ta amince a sanya Shekarau da wasu mutane cikin kunshin Shari’ar sayar da filin makarantar Islamiyyar

Date:

 

 

Babbar kotun shari’ar addinin musulinci dake zaman ta, a Shahuci Kano, ta dage sauraren da’awar shari’ar da iyayen yara da malaman Makarantar Imam Malik Bin Anas Littahafizul Qur’an wattarbiyya Wat Ta’alim, dake unguwar Sabuwar Gandu a karamar hukumar Kumbotso, kan karar da suka shigar da wasu mutane 8 , bisa zargin siyar da filin da tsohon sanatan Kano ta tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau, ya bayar a matsayin wakafi don gina makarantar isilamiya.

A zaman kotun na ranar Talata, lauyan masu kara barista Ahamed Makari, ya roki kotun ta ba su damar sanya sunan tsohon Sanatan Kano ta tsakiya, Mallam Ibrahim Shekarau , da kuma wadanda suka zama wajibi a sanya su, a kunshin shari’ar dan sadasu da sammaci a gajeren lokaci don su gabatar da da’awarsu.

Talla

Luyan da ke tsayawa wadanda aka karar, Barista Shehu Mai-Yaki, bai yi suka ba, kan rokon lauyan masu karar.

Alkalin kotun mai shari’a Mallam Muhammad Sani Ibrahim, ya amince da rokon.

Har yanzu ban ga dokar da ta baiwa jami’an tsaro damar yiwa wanda ake zargi bidiyo ba – Dr. Nuhu Musa Idris

Iyayen yaran da malamansu, sun cika harabar kotun don ganin yadda zata kasance a matsayinsu na masu kara.
A bangaren lauyan wadanda aka yi kara Barista Shehu Mai-yaki, ya ce ba zai yi magana da manema labarai ba har sai ya nemi izini daga na sama dashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...