Madakin Gini ya yiwa Kwankwaso martani kan batun tsige shi daga muƙaminsa na majalisa

Date:

 

Mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai, Ali Madakin Gini ya baiyana cewa abin dariya ne a ce waɗanda ba ƴan jam’iyyar NNPP ba su yi yunƙurin cire shi daga muƙamin sa.

A wata tattaunawa da jaridar DAILY NIGERIAN, Madaki ya zargi jagoran NNPP na ƙasa, Rabi’u Kwankwaso da kitsa yunƙurin tsige shi daga muƙaminsa.

A cewar sa, ya za a yi waɗanda shugabancin jam’iyya na ƙasa ya kore su, kuma su sami ikon cire wani daga muƙamin sa, inda ya ƙara da cewa wani yunkuri ne na wasu da su ke rawa da bazar Kwankwaso “kuma su ke ganin cewa duk abinda ya faɗa ta zauna.”

Talla

“Waɗanda su ka rattaba hannu a takardar ba yan jam’iyyar NNPP ba ne. Kwanan nan kotu ta kori shugabancin jam’iyar bangaren Kwankwaso.

‘Yan majalisar NNPP sun amince da tsige Ali Madaki tare da bayyana wanda zai maye gurbinsa a mukaminsa na majalisa

“Saboda haka wannan su na bata wa kan su lokaci ne kawai saboda kwanan nan kotu to kori shi kansa Kwankwason daga jam’iyyar. Amma ka san dole su rika rawa da bazar Kwankwaso,” in ji Madaki.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito wasu yan majalisar tarayya na jam’iyyar NNPP 15 daga cikin 18 sun nemi a tsige Madakin gini daga muƙaminsa na mataimakin shugaban marasa rinjaye.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...