Da dumi-dumi: Matatar mai ta Fatakwal ta fara aiki

Date:

Kamfanin mai na Nigeria ya bayyana cewa matatar mai ta garin Fatakwal da ke Jihar Rivers ta fara aikin sarrafa mai.

Wannan bayani ya fito daga bakin Babban Jami’in Hulɗa da Jama’a na Kamfanin Mai na Ƙasa (NNPCL), Femi Soneye.

Talla

“A yau an samu gagarumin nasara ga Najeriya yayin da Matatar Fetur ta Port Harcourt ta fara sarrafa mai a hukumance. Wannan matakin ya ƙaddamar da sabon babi na cin gashin kai a fannin makamashi da haɓaka tattalin arziki a ƙasarmu,” in ji Soneye a ranar Talata.

“Muna taya Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Hukumar Gudanarwa ta NNPC, da kuma jagorancin Mele Kyari murna bisa irin namijin ƙoƙarinsu a wannan aikin juyin juya hali. Tare, muna canza makomar makamashin Najeriya!”.

Madakin Gini ya yiwa Kwankwaso martani kan batun tsige shi daga muƙaminsa na majalisa

Soneye ya kuma bayyana cewa za a fara lodin man fetur a cikin motocin daukar kaya a ranar Talata (yau), tare da ƙara da cewa NNPCL tana kuma yin aiki tukuru don dawo da Matatar Fetur ta Warri nan ba da jimawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...