Kidan Gangi ya Tunzura Wani Matashi ya Hallaka Kansa a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Wani matashi mai suna Yusuf Garba, ɗan kimanin shekaru 35 a jihar Kano ya daɓa wa kansa wuƙa, inda haka yayi sanadiyyar mutuwarsa Sakamakon sauraron kiɗan gangi.

Rundunar ’yan sandan Kano ta ce matashin ɗan garin Ɓutu-ɓutu da ke Ƙaramar Hukumar Rimin Gado ya daɓawa kansa wuƙa har lahira bayan da ya kunna kiɗan gangi.

Talla

Kakakin rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana a shafinsa na Facebook, cewa matashin ya koma ga Mahaliccinsa ne bayan daɓawa kansa wuƙa a ciki da ƙafa, dalilin shaukin kiɗan da ya ɗebe shi.

Inganta Ilimi: Jam’iyyar adawa ta YPP ta Yabawa Gwamnan Jihar Kano

Ga sakon da Kiyawa ya wallafa

SHAUKIN KIDAN GANGI

” Yusuf Garba, dan shekaru 35 dake Garin Butu Butu, Karamar Hukumar Rimin Gado, Jihar Kano, ya kunna kidan gangi a waya, wanda kidan ya zabureshi da cakawa kansa wuka a kafa da ciki har lahira. Jama’a muna kiyaye rayuka da lafiyarmu”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...