Kidan Gangi ya Tunzura Wani Matashi ya Hallaka Kansa a Kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Wani matashi mai suna Yusuf Garba, ɗan kimanin shekaru 35 a jihar Kano ya daɓa wa kansa wuƙa, inda haka yayi sanadiyyar mutuwarsa Sakamakon sauraron kiɗan gangi.

Rundunar ’yan sandan Kano ta ce matashin ɗan garin Ɓutu-ɓutu da ke Ƙaramar Hukumar Rimin Gado ya daɓawa kansa wuƙa har lahira bayan da ya kunna kiɗan gangi.

Talla

Kakakin rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana a shafinsa na Facebook, cewa matashin ya koma ga Mahaliccinsa ne bayan daɓawa kansa wuƙa a ciki da ƙafa, dalilin shaukin kiɗan da ya ɗebe shi.

Inganta Ilimi: Jam’iyyar adawa ta YPP ta Yabawa Gwamnan Jihar Kano

Ga sakon da Kiyawa ya wallafa

SHAUKIN KIDAN GANGI

” Yusuf Garba, dan shekaru 35 dake Garin Butu Butu, Karamar Hukumar Rimin Gado, Jihar Kano, ya kunna kidan gangi a waya, wanda kidan ya zabureshi da cakawa kansa wuka a kafa da ciki har lahira. Jama’a muna kiyaye rayuka da lafiyarmu”.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...