Kotu ta hana CBN riƙe kuɗin ƙananan hukumomin Kano

Date:

Daga Sani Sani Idris

 

Babbar Kotun Jihar ta hana Babban Bankin Nijeriya (CBN) da Gwmanatin Tarayya riƙe kuɗaɗen ƙananan hukumomin jihar 44 na wata-wata.

Kotun ta bayar da umarnin wucin gadin ne ga Gwamantin Tarayya da hukumominda ma’aikatunta, bayan ƙarar da Ƙungiyar Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi ta Nijeriya (NULGE) da wasu masu kishin Jihar Kano.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a Ibrahim Musa Muhammad, ya ba da umarnin ne ga CBN da Hukumar Rabon Kudaden Shiga na Kasa da Kuma Akanta-Janar na Tarayya kan tabawa, rikewa ko jinkirin sakin kudaden kananan hukumomin na jihar Kano.

Talla

Ya ba da umarnin ne kan karar da masu karar suka nuna damuwa cewa game da yiwuwar rikewa ko jinkirin kudaden kananan hukumomin ko wani bangaren kudaden.

Cire Kwamishiniyar jin ba zai Haifawa gwamnatin Kano da mai Ido ba – Shugaban APC Integrity

Alkalin ya kuma umarci hukukumomin gwamantin da wakilansu da kada su kuskura su yi duk wani nau’in katsalandan kan kudaden kananan hukumomin.

Daga nan ya dage zaman zuw ranar 21 ga watan nan na Nuwamba, 2024.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...