Zaɓen Ƙananan Hukumomi: An Samu Jinkirin Raba Kayan Zaɓe A Kaduna

Date:

 

 

Jinkirin isar kayan zaɓe da ma’aikata ya haifar da tsaiko a zaɓen ƙananan hukumomin Jihar Kaduna da ke gudana a ranar Asabar.

An shirya fara zaɓen ne da misalin ƙarfe 8 na safe, amma har bayan ƙarfe 10 na safe, ba a fara kaɗa ƙuri’a ba a mafi yawan rumfunan zabe.

Talla

Wakilinmu da ya ziyarci wurare da dama a unguwannin Tudun Wada Badiko da Magajin Gari da Unguwar Sarki, inda ya lura cewa ba a kai kayan zaɓe zuwa rumfunan zaɓe ba.

An tsara fara yin rijista da kaɗa kuri’a da misalin ƙarfe 8:30 na safe kuma a kammala da ƙarfe 2 na rana.

Kotu ta ki amincewa da umarnin dakatar da zaben kananan hukumomin Kano

Tsohon Kansila na Unguwar Sarki, Zubairu Shan’una, ya ce, “Har yanzu muna nan muna jiran kayan zaɓe su iso.

“Kamar yadda ka sani, zaɓen ya kamata ya fara da ƙarfe 8:30 na safe, amma har ƙarfe 10 na safe kayan zaɓe ba su iso Unguwar Sarki ba,” in ji shi.

Malam Idris, wakilin jam’iyya a rumfar zaɓe ta Makarantar Sakandare ta Maimuna Gwarzo da ke Tudun Wada, ya ce ya isa wajen zaɓen da misalin ƙarfe 6:30 na safe.

Talla

Amma a cewarsa ma’aikatan zaɓen ba su isa wajen ba, kuma ba a raba kayan zaɓe ba.

A Magajin Gari, an samu rikici yayin da wakilan jam’iyyu suka yi ƙorafin samun jinkirin rabon kayan zaɓe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...