Kungiyar ‘Yan Wasan Fim ta Najeriya (AGN) ta dakatar da jarumar Nollywood Halima Abubakar saboda zargin bata suna.
A cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a shafinta na Instagram, ta bayyana cewa binciken da aka gudanar tsawon shekaru biyu ta hannun kwamitin da aka kafa ya nuna cewa Halima ta bata sunan wasu daga cikin abokan aikinta.
“Biyo bayan cikakken rahoton bincike na kwamitin Bincike na Musamman da aka kafa don gudanar da bincike a karkashin kasa game da ayyukan wasu shafukan yanar gizo tun daga 2022,” AGN ta rubuta.
Bincike ya gano adadin yawan yan Nigeria da suka talauce a bana
“Bayan shekaru biyu na bincike mai zurfi, Kwamitin ya gano cewa Halima Abubakar ce ke da alhakin dukkan bayanan bata suna na mambobinmu, abokan huldarmu, da masu tallafa mana, musamman labaran da suka shafi alakar saduwa da aka alakanta da mutane masu kima a cikin al’umma daga masana’antar.”
Kungiyar ta ce, duk da dakatarwar da aka yi wa Halima, har yanzu za ta fuskanci matakan ladabtarwa.
“Saboda haka, Halima Abubakar an dakatar da ita ba tare da iyaka ba daga Kungiyar ‘Yan Wasan Fim ta Najeriya. Za ta fuskanci Kwamitin Ladabtarwa na Kasa don yanke hukuncin da ya dace. A lokacin wannan dakatarwar, ba a ba ta damar shiga cikin kowanne irin aiki na AGN ko kuma aikin fim.”