Abun da Baffa Babba ya yiwa matasan Kano zai kara musu kwarin gwiwa – Sharu Sani Madigawa

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Wani malami a Kano mai suna sharu sani Madigawa ya yabawa Shugaban hukumar ingantuwar aiyukan ta kasa Baffa Babba Dan’agundi Bisa yadda ya dauki yan jihar kano ya basu mukamai daban-daban a Ofishinsa.

” Ina yabawa Baffa Babba Dan’agundi saboda ya yi abun da ya dace na baiwa Matasa mukamai , saboda irin gudunmawar da suka bayar yayin zaɓen da ya gabata, hakan zai karawa matasa kwarin gwiwar shiga Siyasa”.

Talla

Sharu Madigawa ya bayyana hakan ne yayin da ya gana da wakilin jaridar kadaura24.

Rikicin NNPP: Gwamnan Kano ya Bijirewa Umarnin Kwankwaso, na cire wasu jami’an gwamnati

‘ Ina mafani da wannan dama wajen taya Nabila Bature murna Bisa mukamin da Baffan ya bata na wakiliyarsa a Kano ta yadda zata rika sanya idanu akan duk abun da ya shifi yan kungiyoyin Support Group”. Inji sharu madigawa

Talla

Ya ce yana da yakinin Nabila Bature zata yi aikin ta yadda ya dace domin ciyar da jam’iyyar APC gaba a jihar kano, da kuma kyautata alaka tsakanin Baffa Babba Dan’agundi da yan kungiyoyin Support Group.

Talla

Ya bukace ta da ta zama mai gaskiya da rikon Amana, Sannan ta yi aiki tukuru domin sauke nauyin da Baffa Babba Dan’agundi ya dora mata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...