Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Wani malami a Kano mai suna sharu sani Madigawa ya yabawa Shugaban hukumar ingantuwar aiyukan ta kasa Baffa Babba Dan’agundi Bisa yadda ya dauki yan jihar kano ya basu mukamai daban-daban a Ofishinsa.
” Ina yabawa Baffa Babba Dan’agundi saboda ya yi abun da ya dace na baiwa Matasa mukamai , saboda irin gudunmawar da suka bayar yayin zaɓen da ya gabata, hakan zai karawa matasa kwarin gwiwar shiga Siyasa”.
![](https://kadaura24.com/wp-content/uploads/2024/10/IMG-20240925-WA0001-300x225.jpg)
Sharu Madigawa ya bayyana hakan ne yayin da ya gana da wakilin jaridar kadaura24.
Rikicin NNPP: Gwamnan Kano ya Bijirewa Umarnin Kwankwaso, na cire wasu jami’an gwamnati
‘ Ina mafani da wannan dama wajen taya Nabila Bature murna Bisa mukamin da Baffan ya bata na wakiliyarsa a Kano ta yadda zata rika sanya idanu akan duk abun da ya shifi yan kungiyoyin Support Group”. Inji sharu madigawa
![](https://kadaura24.com/wp-content/uploads/2024/09/IMG-20240926-WA0041-212x300.jpg)
Ya ce yana da yakinin Nabila Bature zata yi aikin ta yadda ya dace domin ciyar da jam’iyyar APC gaba a jihar kano, da kuma kyautata alaka tsakanin Baffa Babba Dan’agundi da yan kungiyoyin Support Group.
![](https://kadaura24.com/wp-content/uploads/2024/10/IMG-20241013-WA0026-211x300.jpg)
Ya bukace ta da ta zama mai gaskiya da rikon Amana, Sannan ta yi aiki tukuru domin sauke nauyin da Baffa Babba Dan’agundi ya dora mata.