Gwamnan Kano ya bada tallafin Naira miliyan 100 ga wadanda gobarar kasuwar kantin kwari ta shafa

Date:

Daga Kamal Yahaya Zakaria

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf a madadin gwamnatin jihar Kano ya sanar da bayar da tallafin Naira Miliyan Dari ga wadanda gobara ta shafi shagunansu a cikin shahararriyar kasuwar Kantin Kwari a kwanakin baya.

Gwamnan ya sanar da bayar da tallafin ne a lokacin da ya jagoranci manyan jami’an gwamnati Inda suka je kasuwar domin yiwa yan kasuwar jaje a ranar alhamis.

Talla

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24 , ya ce gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna kaduwarsa Kan Iftila’in da ya sami yan kasuwar ta kwari.

Gwamnan ya ce tallafin ba diyya ba ne ga asarar da aka yi Sanadiyar a gobarar, a’a, an bada shi ne domin rage radadin ga wadanda gobara ta yiwa barna.

Sabon Rikici ya balle tsakanin yan majalisar tarayya na jam’iyyar NNPP a Kano

Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bada tabbacin gwamnatin jihar Kano zata inganta yanayin kasuwar domin samun yanayi mai kyau da saukin kasuwanci a kasuwa ta hanyar sanya fitulu masu amfani da hasken rana; gyaran hanyoyin cikin kasuwar, gina magudanun ruwa da samar da rijiyoyin burtsatse da sauran su.

Ya roki shugabannin kasuwar da su bullo da shirye-shiryen da za su taimaka wa dubun dubatar ’yan kasuwar don gudanar da harkokinsu na yau da kullum ba tare da tangarda ba tare da tabbatar da cewa gwamnatin jihar za ta yi duk abin da ya dace domin Kano ta ci gaba da rike matsayinta na cibiyar kasuwanci a Arewacin Najeriya wasu kasashen yammacin Afirka.

Talla

Tun da farko, Manajan Daraktan Hukumar Kula da Kasuwar Kantin Kwari, Alhaji Hamisu Sa’ad Dogon Nama ya ce shaguna 29 ne gobarar ta kone, kuma ya yaba da yadda jami’an kashe gobara da sauran masu ruwa da tsaki suka yi gaggawar daukar matakin dakile yaduwar gobarar .

Shugaban Kwamitin Dattawan Kasuwa, Alhaji Sabu’u ​​Bako ya gode wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa yadda ya nuna damuwa da halin da ‘yan kasuwar ke ciki, ya kuma yi kira ga Gwamnan da ya taimaka wajen magance wasu matsalolin da ke kawo cikas a kasuwar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Magance sheye-shaye ne kadai zai kawo karshen matsalar tsaro da talauci a Nugeria – Shugabar LESPADA

Daga Usman Usman   Ambassador Maryam Hassan shugabar kungiyar wayar da...

‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers Ta Mayar Da Martani Kan Sauke Alhaji Usman Daga Mukamin Wazirin Gaya

Daga Isa Ahmad Getso ‎ ‎Kungiyar APC Patriotic Volunteers ta bayyana...

Rahoto: An kwantar da Buhari a ICU a Landan

  Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin...

Kacibus: A karon farko an hadu tsakanin Gwamnan Abba da Sarki Aminu Ado a Madina

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   A karon farko an hadu tsakanin...