Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Aikin Tsaftar Muhalli A Ƙananan Hukumomin Jihar

Date:

Daga Abubakar Yakubu

 

Kwamishinan Ma’aikatar Gidaje da Muhalli na jihar Bauchi, Rt. Honarabul Ɗanlami Ahmed Kawule (Barden Arewan Bauchi), ya ƙaddamar da aikin tsaftar Muhalli a ƙananan Hukumomin Jihar Ashirin.

Barden Arewan Bauchi ya ƙaddamar da aikin ne a Unguwar Kobi, bisa cikakken goyon bayan Gwamnan Jihar Bauchi Sanata Bala Abdulkadir Muhammad, domin tabbatar da tsafta da Lafiyar al’ummar jihar.

Talla

Manufar ƙaddamar da aikin shine, tabbatar da tsafta a lungu da saƙo na jihar, Samarwa Matasa hanyar dogaro da kansu, ƙara samar da ayyukan ci-gaba, ciki harda gyaran Masallacin Unguwar Kobi, harma da gyara magudanan ruwa domin yin kandagarkin faruwar ambaliyar ruwa.

A cewar Kwamishinan, “Duba da yadda Gwamnan Bala Muhammad ya bawa tsaftar Muhallin al’umma muhimmanci, shiyasa muka himmatu wajen gudanar da irin wannan aiki akai-akai, domin ganin cewa al’umma suna yi kamar yadda aka tsara”.

Gwamnatin Bauchi ta kammala gina gidaje 2000 domin rabawa al’umma – Kwamishinan Muhalli da Gidaje

Harma ya ce manufar shirin shine, tabbatar da tsaftar Muhalli, ƙarfafawa al’umma gwuiwar tsafta ce yankunan su, samarwa Matasa guraben aiki, samar da ƙarin ayyukan ci-gaba dama yin kandagarkin faruwar ambaliyar ruwa.

A ƙarshe sanarwar da Mashawacin Gwamnan akan kafafen sada zumunta, Alhaji Nuru Abdullahi (Baban Zahra), ya aiko wa jaridar GTR Hausa ta ce, Gwamnatin jihar zata ci-gaba ƙoƙari wajen inganta lafiya da samar da kyakykyawan Muhalli ga talakawan jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...