Yanzu-yanzu: Kotu ta dakatar da zaben kananan hukumomin Kano

Date:

Daga Mustapha Ibrahim

 

Babbar kotun tarayya mai zamanta Kano karkashin jagorancin Mai Shari’a S. A Amobeda ta baiwa hukumar zabe mai zaman kanta ta Kano wato KANSIEC umarnin dakatar da duk wasu shirye-shirye gudanar da zaben kananan hukumomin jihar da ta shirya yi a watan gobe.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito hukumar zaben ta KANSIEC ta shirya gudanar da zaben kananan hukumomin jihar kano a ranar 26 ga watan October mai zuwa.

Talla

Wani Hon. Aminu Aliyu Tiga da jam’iyyar APC ne suka shigar da karar tare da neman kotun da ta dakatar da zaben har sai ta saurari kundarin Shari’ar.

A karar da suka shigar sun kalubalanci hukumar zaben Kano kan taka ƙa’idojin shirin gudanar da zaɓe da kuma sanya kudin siyan fom ɗin shiga zaɓe, wanda APC ta hannun Hon. AA Tiga yace bai gamsu da yadda aka shirya shiga zaben ba.

El-Rufa’i ya magantu kan dawo da Sarki Sanusi II gadon sarautar Kano

Kotun ta bada umarnin dakatar da duk wani shiri na shiga zaɓen har sai an fara shari’ar.

Kotun ta kuma ce zata fara sauraren karar ne a ranar 04 ga watan October mai kamawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kisan ɗalibai a Kano: Kwamitin Malamai da Iyayen yara na jihar ya nuna damuwarsa

Daga Abdulhamid Isah D/Z Malam Salisu Abdullahi shugaban kwamitin malamai...

Hakikanin halin da gwamnan Katsina yake ciki, bayan wani hatsari

  Rahotanni daga Katsina na cewa gwamnan jihar Katsina Dikko...

Zargin almundahana: ICPC ku fita daga harkokin Siyasar Kano – Kungiyar Ma’aikatan KANSIEC

Daga Hafsat Abdullahi Darmanawa   Kungiyar ma'akatan wucin gadi da suka...

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...