Tinubu ya fi ƙarfin satar dukiyar Najeriya — Minista

Date:

 

Ƙaramin Ministan Harkokin Matasa, Ayodele Olawande, ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya fi ƙarfin ya saci dukiyar Najeriya.

Da yake jawabi a wajen taron Ƙungiyar Haɗin Kan Ma’aikata (JUNC), a Ma’aikatar Harkokin Ci Gaban Matasa a Abuja, Olawande, ya yi kira ga ‘yan Najeriya su ƙara haƙuri da halin da ake ciki a ƙasar nan.

Ya yi alƙawarin cewa nan ba da daɗewa ba za a ga sauye-sauyen da suka dace.

Dalori ya taya al’ummar Musulmi Murnar Bikin Mauludin Annabi S A W

Ya bayyana cewa Tinubu mutum ne mai arziƙi, kuma ba shi da sha’awar satar dukiyar ƙasar nan.“Tinubu ba talaka ba ne; ya jima da samun arziƙi, don haka ba shi da sha’awar satar dukiyar Najeriya,” in ji Olawande.

Ya kuma bayyana cewa shugabanci ba abu ne da zak dauwama ba, abin da ya fi muhimmanci shi ne irin gudunmawar da shugabanni suka bayar a lokacin da suke kan mulki.

Maulidi: Minista T Gwarzo ya bukaci al’ummar Musulmi su rika koyi da halayen Annabi S A W

Tinubu wanda ya yi gwamna har sau biyu kuma ya taɓa zama Sanata, yana da hannun jari da yawa a wurare da suka haɗa da gidaje, aikin jarida, da harkar shaƙatawa.

A wani taro kafin rantsar da Tinubu, uwargidansa, Oluremi Tinubu, ta ce iyalanta ba sa buƙatar dukiyar Najeriya don azurta kansu.

Ta yi alƙawarin cewa za su yi aiki domin inganta ƙasar nan don amfanin kowa da kowa.

Daily trust

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...