Zaɓen kananan hukumomin Kano: APC ta fadi matsayarta

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Jam’iyyar APC a jihar Kano tace za ta shiga zaɓen ƙananan hukumomi da za a gudanar a ranar 26 ga watan Oktoba mai zuwa.

A sanarwar da kakakin jam’iyyar, Hon. Ahmad S Aruwa ya fitar yace bayan karbar rahoton kwamitin da ya tattara shawararwari don shiga zaben, jam’iyyar ta yanke hukunci shiga a matsayinta Na jam’iyya mai mulki a Najeriya.

Gwamnatin Kano ta dakatar da tsawaita wa’adin ma’aikata 4,000 da Ganduje ya yi

Sanarwar ta kuma umarci dukkanin masu sha’awar takarar su kai takardar nuna sha’awa ga ofishin jam’iyyar dake kananan hukumomi tun daga ranar 12 zuwa 14 ga watan Satumba.

Idan za’a iya tunawa a kwanakin baya jam’iyyar APC ta jihar kano ta kafa wani kwamiti karkashin jagorancin Rabi’u Sulaiman Bichi, domin su duba yiwuwa jam’iyyar ta shiga zaben ko kar ta shiga.

 

Daga karshe dai a jiya laraba kwamiti ya mika rahotonsa, kuma ga shi a yau jam’iyyar ta amince zata shiga a fafata da ita a zaɓen shugabannin kananan hukumomin dake tafe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...