Zaɓen Kano: NDLEA ta fitar da sakamakon yan takara 20 da aka yiwa gwajin shan kwaya

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ta ce sun yiwa mutane 20 da ke neman kujerar shugabannin kananan hukumomi a jihar Kano gwajin kwaya da sauran kayan maye gabanin zaben kananan hukumomi da ke tafe.

Kwamandan NDLEA a jihar, Abubakar Idris Ahmad, ya ce masu neman takarar da jam’iyyar NNPP mai mulki ta gabatar a jihar an yi musu gwajin kwayoyi har ma da hotar iblis da dai sauransu.

Jerin sunayen yan takara 38 da NNPP ta tsayar a zaɓen shugabannin kananan hukumomin Kano

Ahmad ya bayyana cewa, duk da cewa babu mace ko daya da suka yiwa gwajin ya zuwa yanzu, amma ana ci gaba da gudanar da aikin tantancewar, kuma ana sa ran za a yi wa sauran ‘yan takarar gwajin kafin hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano (KANSIEC) ta yi musu nata.

Shugaban hukumar ta NDLEA a Kano ya ce duk cikin wadanda suka tantance din ba a sami ko mutum daya mai shan kwaya ko wani Abu mai bugarwa ba.

Idan dai za a iya tunawa, hukumar ta KANSIEC ta tsayar da ranar 26 ga Oktoba, 2024, inda za a fafata a kujerun shugabanni 44 da na kansiloli 484.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...