Muna addu’ar Allah Ya dawo mana da kai cikin mu -APC ga Kawu Sumaila

Date:

 

 

Jam’iyyar adawa ta APC a jihar Kano ta nuna fatan Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila ya dawo gidan sa na siyasa da ya bari.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa Sanata Sumaila ya fice daga APC ne a gabanin zaɓen 2023, inda ya sauya sheka zuwa jam’iyyar adawa (a wancan lokacin) ta NNPP kuma ya tsaya takara a nan har ya ci zaɓe.

Karin Farashin Man Fetur da VAT Zai Karawa Yan Nigeria Matsin Rayuwa -Atiku ga Tinubu

Sai dai kuma a yayin kaddamar da rabon kayan abinci da shugaban kasa ya bayar a rabawa talakawa a Kano a yau Lahadi, kakakin jam’iyyar APC a Kano, Ahmed Aruwa, ya yi fatan Kawu Sumaila ya dawo jam’iyyar ta su.

Yayin da ya ke yi mika sannu da zuwa ga manyan baki da su ka halarci taron, Aruwa, cikin barkwanci ya ce “Sanata Kawu Sumaila, Sanatan alheri. Allah Ya maida koko masaki. Allah Ya dawo mana da kai jam’iyyar APC,”

Zaɓen 2027: Kwankwaso Ya Bugi Kirji

Bayan da Aruwa ya fadi wannan kalamai, sai gurin ya rude da shewa da cewa “ameen”.

Sai dai kuma Daily Nigerian Hausa ta gano cewa Aruwa ya baiyana wannan fata ne a kashin kan sa ba da yawun jam’iyyar APC ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...