Muna addu’ar Allah Ya dawo mana da kai cikin mu -APC ga Kawu Sumaila

Date:

 

 

Jam’iyyar adawa ta APC a jihar Kano ta nuna fatan Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Sanata Abdulrahman Kawu Sumaila ya dawo gidan sa na siyasa da ya bari.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa Sanata Sumaila ya fice daga APC ne a gabanin zaɓen 2023, inda ya sauya sheka zuwa jam’iyyar adawa (a wancan lokacin) ta NNPP kuma ya tsaya takara a nan har ya ci zaɓe.

Karin Farashin Man Fetur da VAT Zai Karawa Yan Nigeria Matsin Rayuwa -Atiku ga Tinubu

Sai dai kuma a yayin kaddamar da rabon kayan abinci da shugaban kasa ya bayar a rabawa talakawa a Kano a yau Lahadi, kakakin jam’iyyar APC a Kano, Ahmed Aruwa, ya yi fatan Kawu Sumaila ya dawo jam’iyyar ta su.

Yayin da ya ke yi mika sannu da zuwa ga manyan baki da su ka halarci taron, Aruwa, cikin barkwanci ya ce “Sanata Kawu Sumaila, Sanatan alheri. Allah Ya maida koko masaki. Allah Ya dawo mana da kai jam’iyyar APC,”

Zaɓen 2027: Kwankwaso Ya Bugi Kirji

Bayan da Aruwa ya fadi wannan kalamai, sai gurin ya rude da shewa da cewa “ameen”.

Sai dai kuma Daily Nigerian Hausa ta gano cewa Aruwa ya baiyana wannan fata ne a kashin kan sa ba da yawun jam’iyyar APC ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...