YANZU-YANZU: Tinubu ya magantu kan karin farashin man fetur Nigeria

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya magantu kan karin kudin mai da aka yi a farkon makon nan

Karin kudin man dai yasa ana siyar da lita daya daga Naira 897 a gidajen man NNPC, maimakon 617 da ake siyarwa a baya.

Yayin da a gidajen man ‘yan kasuwa ake siyar da duk Lita kan Naira 1, 200.

Gwamnatin tarayya ta fara sayar da shinkafarta akan Naira 40,000

Da yake bayani yayin ganawa da ‘yan Nijeriya a birnin Beijing na China, Tinubu ya ce karin kudin man “Mataki ne mai tsauri wanda ba a saba gani ba” da ya zama dole don ci gaban Nijeriya.

A sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasar, Ajuri Ngelale ya fitar, ya ambato shi na cewa matakan da gwamnatinsa ke dauka na daga cikin dabarun dora tattalin arzikin Nijeriya bisa turba.

Kotu ta tusa keyar alƙalin bogi zuwa gidan yari a Kano

Sai dai al’ummar Nigeria na ci gaba da kokawa da sabbin manufofin shugaban ƙasar, wadanda suka sanya ƙasar cikin mawuyacin.

Tinubu ya ce nan ba da jimawa yan Nigeriya zasu Fara amfana da sabbin manufofin da aka fito da su don inganta tattalin arzikin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...