Iftila’i: Bayan wani mummunan hadari al’umma sun rufe titin Kano zuwa Zaria

Date:

Daga Aminu Bala Modobi

 

Rahotanni na nuni da cewa al’ummar garin Imawa dake karamar hukumar Kura a jihar Kano sun rufe titin Kano zuwa Zaria.

Kadaura24 rawaito cewa wasu mazauna garin sun bayyana cewa sun dauki matakin rufe hanyar ne sakamakon yadda wata mota ta buge wasu mutane da suka taso daga Sallar Juma’a.

Motar yayin da take tsaka da tafiya ta kwacewa direban, inda ta kutsa kai tareda danne Massallatan yayinda aka gaggauta kai wadanda suka jikkata zuwa asibiti domin kulada lafiyar su.

 

An rawaito cewa nan take mutane 7 suka rasa rayukansu, yayin da wasu kuma suka jikkata.

Mafi Ƙarancin Albashi: Majalisar dokokin Kano ta amince da kwarya-kwaryar kasafin kuɗi na N99b

Tuni dai wasu daga cikin mutanen garin suka sanya wa motar da ta buge masallatan wuta inda suka ƙone ta ƙurmus.

“Sun sanya wa motar wuta ne a kan titi sannan suka kashe kan hanyar sakamakon zargin bige musu ƴan uwa da wata mota ta yi. Inda mutane 7 suka mutu sakamakon hatsari”, in ji wata majiya dake wurin

Wani matafiyi dake hanyar ya shaida mana cewa fiye da awa uku ke nan hanyar Kano zuwa Zaria take a rufe sakamakon wancan hadari.

Kotu ta tusa keyar alƙalin bogi zuwa gidan yari a Kano

Majiyar ta ƙara da cewa; “masu motoci dai sun yi jungum-jungum, inda lamarin ya shafi dubban matafiya. Komai ya tsaya cik ba abin da ke motsi.”

Idan za’a iya tunawa makwanni shida da suka gabata, wata mota ta buge mutane da dama a lokacin da suke sallah Juma’a a dai garin na Imawa dake karamar hukumar

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...