Daga Aliyu Danbala Gwarzo
Kamfanin mai na Najeriya NNPC ya bayyana cewa man fetur a ƙasar shi da kansa ne zai rika yiwa kansa farashi a kasuwa.
Mataimakin shugaban sashin hako mai na kamfanin Mista Adedapo Segun ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da shi a wani Shirin na gidan talabijin na TVC ranar alhamis.
Ya ce kundin tsarin mulki bai ƙayyade waɗanda za su tsayar da farashin man fetur ba.
Yaki da cin hanci: Kungiyar mata Yan jarida ta karrama Muhuyi Magaji
A cewarsa, sashi na 205 da ya kafa kamfanin, ya bashi damar sakin fetur don nemawa kansa farashi a kasuwa.
Ya ƙara da cewa dangane da tsadarsa da mutane ke kokawa, batu ne da ya shafi chanjin kudaden kasashen waje.
” Ba wani mai lafiyayen hankali da zai ji dadi saboda tsadar man fetur kawai ba yadda zamu yi ne, yanzu ba mu da ikon ƙayyade farashin man fetur a Nigeria”.
Amma ya ce su na ƙoƙarin su da dilallan man na ƙasa don ganin an magance karancinsa.
Kungiyar One Voice Initiative ta nada sabbin shugabanninta na kasa
Kuma ya sake tabbatarwa da ƴan Najeriya cewar, nan da kwana ƙalilan za a kawo ƙarshen matsalar ƙarancin man baki ɗaya.
Dan gane da batun man fetur na matatar Ɗangote kuwa, Segun ya ce nan da 15 ga watan satumba za a Fara ganin man a kasuwa kamar yadda aka tsara.
A cewar kamfanin, a halin yanzu man fetur na nemawa kansa farashi ne a kasuwa.