Karin Farashin Mai: Ya kamata yan majalisu su takawa NNPC burki – Gidauniyar GCAF

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gidauniyar Tallafawa Mabukata Daga Tushe wato Grassroot Care and Aid Foundation GCAF tayi Kira ga Gwamnatin Tarayya data gaggauta janye Karin kudin da NNPCL tayi a wannan yanayin da ake ciki na tsadar rayuwa Wanda asalinsa dama janye Tallafin man fetur da akayi shine sanadin hakan.

Shugaban Gidauniyar Amb. Auwalu Muhd Danlarabawa shi ne ya bayyana hakan yau ga manema labarai domin nuna damuwa da halin da al’umma ke ciki na tsadar rayuwa da hauhawar farashi dama yawan Mutuwa da ake tayi sanadin rashin abinci.

Matatar Dangote za ta samar da lita man fetur miliyan 25 a kowace rana – NMDRA

Amb. Auwalu Muhd Danlarabawa ya Kara da cewa wajibi ne yan majalisu su yi wani abu akan wannan al’amari dare da Gwamnonin da suke Jagorancin al’ummar kasa indai da gaske suke dimokradiyya akeyi.

Idan har baa dauki mataki ba a wannan yanayi to gaskiya alama ta nuna cewar shugabannin da muke dasu ba Imani da tausayin al’ummar kasa a tare dasu.

Sannan ya Kara da Kira ga Yan kwadago da suyi abinda ya dace a wannan gaba na Kira da a janye ko Kuma a tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...