Karin Farashin Mai: Ya kamata yan majalisu su takawa NNPC burki – Gidauniyar GCAF

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gidauniyar Tallafawa Mabukata Daga Tushe wato Grassroot Care and Aid Foundation GCAF tayi Kira ga Gwamnatin Tarayya data gaggauta janye Karin kudin da NNPCL tayi a wannan yanayin da ake ciki na tsadar rayuwa Wanda asalinsa dama janye Tallafin man fetur da akayi shine sanadin hakan.

Shugaban Gidauniyar Amb. Auwalu Muhd Danlarabawa shi ne ya bayyana hakan yau ga manema labarai domin nuna damuwa da halin da al’umma ke ciki na tsadar rayuwa da hauhawar farashi dama yawan Mutuwa da ake tayi sanadin rashin abinci.

Matatar Dangote za ta samar da lita man fetur miliyan 25 a kowace rana – NMDRA

Amb. Auwalu Muhd Danlarabawa ya Kara da cewa wajibi ne yan majalisu su yi wani abu akan wannan al’amari dare da Gwamnonin da suke Jagorancin al’ummar kasa indai da gaske suke dimokradiyya akeyi.

Idan har baa dauki mataki ba a wannan yanayi to gaskiya alama ta nuna cewar shugabannin da muke dasu ba Imani da tausayin al’ummar kasa a tare dasu.

Sannan ya Kara da Kira ga Yan kwadago da suyi abinda ya dace a wannan gaba na Kira da a janye ko Kuma a tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...