Karin Farashin Mai: Ya kamata yan majalisu su takawa NNPC burki – Gidauniyar GCAF

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gidauniyar Tallafawa Mabukata Daga Tushe wato Grassroot Care and Aid Foundation GCAF tayi Kira ga Gwamnatin Tarayya data gaggauta janye Karin kudin da NNPCL tayi a wannan yanayin da ake ciki na tsadar rayuwa Wanda asalinsa dama janye Tallafin man fetur da akayi shine sanadin hakan.

Shugaban Gidauniyar Amb. Auwalu Muhd Danlarabawa shi ne ya bayyana hakan yau ga manema labarai domin nuna damuwa da halin da al’umma ke ciki na tsadar rayuwa da hauhawar farashi dama yawan Mutuwa da ake tayi sanadin rashin abinci.

Matatar Dangote za ta samar da lita man fetur miliyan 25 a kowace rana – NMDRA

Amb. Auwalu Muhd Danlarabawa ya Kara da cewa wajibi ne yan majalisu su yi wani abu akan wannan al’amari dare da Gwamnonin da suke Jagorancin al’ummar kasa indai da gaske suke dimokradiyya akeyi.

Idan har baa dauki mataki ba a wannan yanayi to gaskiya alama ta nuna cewar shugabannin da muke dasu ba Imani da tausayin al’ummar kasa a tare dasu.

Sannan ya Kara da Kira ga Yan kwadago da suyi abinda ya dace a wannan gaba na Kira da a janye ko Kuma a tsunduma yajin aikin sai baba ta gani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...