Bankada: Gwamnatin Sakoto za ta gyara ‘bohol’ 25 kowacce daya akan miliyan 48

Date:

 

 

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, na shan suka kan aikin da bayar na gyaran rijiyoyin burtsatse 25 a kan kudi Naira biliyan daya da miliyan 200.

Jakan na nufin za a kashe Naira miliyan 48 a kan kowace rijiyar burtsatse guda daya.

Jama’a na suka gwamnan kan aikin da ya sanar cewa ya bayar na gyara rijiyoyin burtsatse 25.

Bidiyo sanarwar aikin rijiyoyin burtsatsen da ke yawo a kafofofin sada zumunta ya ba baya da kura, inda jama’a da dama sun tofa albarkacin bakinsu.

Farashin Man Fetur ya yi tashin gwauron zabi a Nigeriya

Wasu da daman sun bayyana cewa kwangilar ta yi tsada wasu kuma suna shagube a kan aikin.

Honarabul Abdullahi Hassan, ya yi shagube kan kwangilar inda ya nemi mutane da cewa, su nema masa kwangilar gyaran bohol daya.

Bello Muhammad ya ce, “kwangilar gyara bohol daya a kan kudi naira miliyan 48 ba abu ne da yake kama hankali ba.

“ya kamata gwamnati ta rika lura musamman da halin matsin rayuwa da ake ciki a kasar nan.”

Matatar Dangote za ta samar da lita man fetur miliyan 25 a kowace rana – NMDRA

Ya yi kira ga “gwamna ya rika duba halin da ake ciki, mutanen da za a gyarawa bohol suna bukatar abinci da magani da hanya.

“Kudin da aka ware a zaton da muke da shi, suna iya samar da abu biyu a cikin abin da ake bukata.

“Amma a kashe makudan kudin a gyaran bohol kamar an barnata kudin.”

Kabiru Ahmad ya ce, “Na kalli bidiyon, domin da aka fada min ban yarda ba, sai da gani da kaina, a gaskiya wannan ita ce kwangila mafi tsada da na sani an bayar a gwamnati.”

Ya ce, “ko samar da bohol da wuya ya wuce a kashe Naira miliyan 10, amma a ce za a yi gyara a miliyan 48, ya kamata gwamnati ta lura a gaba, gaskiya nan an yi kuskure a tunanin da nake da shi.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...