Zanga-zanga: Gaskiyar magana kan sakin Turawan da ake zargi da hannu a ɗaga tutar Rasha a Najeriya

Date:

 

An saki ɗalibai da malamai ƴan asalin ƙasar Poland da aka kama a lokacin da aka yi zanga-zangar tsadar rayuwa, kamar yadda Ministan Harkokin Wajen Poland ya bayyana a ranar Laraba.

Mutum bakwan sun shiga hannu ne a Jihar Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya, “bisa zargin su da hannu a ɗaga tutocin Rasha da ma ita kanta zanga-zangar,” kamar yadda jami’an tsaron Najeriya suka bayyana.

Sai dai hukumomi a ƙasar Poland sun ce waɗanda aka kama ɗin ɗalibai ne na Jami’ar Warsaw da malaminsu, waɗanda “tsautsayi ya kai su inda bai dace ba.”

Ministan Harkokin Wajen Poland, Radoslaw Sikorski ya ce yanzu an sako ɗaliban.

Inganta Haraji: Gwamnatin Kano ta ba da umarnin rufe duk asusun ma’aikatu

“Ina tabbatar da cewa an sako mutanenmu ɗin nan, yanzu haka sun koma Kano sun ci gaba da karatunsu,” kamar yadda Sikorski ya wallafa wani bidiyo a shafi X.

Ya ƙara da cewa nan ba da jimawa za su koma ƙasarsu ta Poland bayan sun kammala karatunsu.

A farkon watan Agusta ne aka gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa a Najeriya, lamarin da ya janyo tashin hankula tare da cece-ku-ce a ƙasar.

Talla
Talla

Rikicin da aka samu a wasu jihohi ya yi sanadin rasa rayuka, lamarin da ya kai ga sanya dokar hana fita.

Wani abu da ya janyo hankali shi ne yadda wasu daga cikin masu zanga-zangar suka riƙa ɗaga tutocin Rasha, abin da ya sa jami’an tsaro suka kama mutane da dama.

Tasirin Rasha na ƙaruwa a yankin yammacin nahiyar Afirka tun bayan juyin mulki da aka samu a ƙasashen Nijar, Burkina Faso da Mali.

Ƙasashen waɗanda yanzu ke ƙarƙashin mulkin sojoji sun fice daga ƙungiyar yankin ta Ecowas, suka kori sojojin Amurka da Faransa da yanke hulɗar dangantaka da ƙasashen Yamma sannan sun kuma suka mayar da hankali wajen ƙarfafa alaƙarsu da ƙasar Rasha.

Mahukuntan Najeriya dai sun bayyana ɗaga duk wata tuta a ƙasar baya ga ta Najeriyar a matsayin laifin cin amanar ƙasa, wanda ɗaya ne daga cikin laifuka mafi girma a ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...