Yanzu-yanzu: Al’amura sun tsaya chak a hanyar Kaduna zuwa Abuja

Date:

Rahotanni da ke zuwa yanzu-yanzu daga titin Kaduna zuwa Abuja na cewa an samu cinkoson ababen hawa wanda ya tsayar da hanyar cak, inda ya sanya matafiya su ka yi cirko-cirko.

Wakilin Kadaura24 da ke kan titiin a halin yanzu ya rawaito cewa, wasu matafiya sun baiyana cewa cinkoson ababen hawan ya faru ne sakamakon faduwar wata babbar mota a dai-dai garin Katari, jihar Kaduna.

Talla
Talla

Wani matafiye ya shaidawa Kadaura24 cewa lamarin ya faru ne tun jiya, lamarin da ya sa ake bin hannu daya,wanda ita ma daga bisa hanyar ta daina biyuwa.

An hangi fasinjoji da masu ababen hawa sun yi cirko-cirko a yayin da hanyar ta tsaya cak ba motsi.

Matafiyan dai, na fatan hukumomin lura da hanyoyi za su kai daukin gaggawa.

Hanyar dai ita ce babbar hanya da matafiya da suka fito daga Kano da Kaduna, Katsina da sauran su ke bi wajen zuwa babban birnin tarayya Abuja da kuma kudancin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...