Yanzu-yanzu: Al’amura sun tsaya chak a hanyar Kaduna zuwa Abuja

Date:

Rahotanni da ke zuwa yanzu-yanzu daga titin Kaduna zuwa Abuja na cewa an samu cinkoson ababen hawa wanda ya tsayar da hanyar cak, inda ya sanya matafiya su ka yi cirko-cirko.

Wakilin Kadaura24 da ke kan titiin a halin yanzu ya rawaito cewa, wasu matafiya sun baiyana cewa cinkoson ababen hawan ya faru ne sakamakon faduwar wata babbar mota a dai-dai garin Katari, jihar Kaduna.

Talla
Talla

Wani matafiye ya shaidawa Kadaura24 cewa lamarin ya faru ne tun jiya, lamarin da ya sa ake bin hannu daya,wanda ita ma daga bisa hanyar ta daina biyuwa.

An hangi fasinjoji da masu ababen hawa sun yi cirko-cirko a yayin da hanyar ta tsaya cak ba motsi.

Matafiyan dai, na fatan hukumomin lura da hanyoyi za su kai daukin gaggawa.

Hanyar dai ita ce babbar hanya da matafiya da suka fito daga Kano da Kaduna, Katsina da sauran su ke bi wajen zuwa babban birnin tarayya Abuja da kuma kudancin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...