Yanzu-yanzu: Al’amura sun tsaya chak a hanyar Kaduna zuwa Abuja

Date:

Rahotanni da ke zuwa yanzu-yanzu daga titin Kaduna zuwa Abuja na cewa an samu cinkoson ababen hawa wanda ya tsayar da hanyar cak, inda ya sanya matafiya su ka yi cirko-cirko.

Wakilin Kadaura24 da ke kan titiin a halin yanzu ya rawaito cewa, wasu matafiya sun baiyana cewa cinkoson ababen hawan ya faru ne sakamakon faduwar wata babbar mota a dai-dai garin Katari, jihar Kaduna.

Talla
Talla

Wani matafiye ya shaidawa Kadaura24 cewa lamarin ya faru ne tun jiya, lamarin da ya sa ake bin hannu daya,wanda ita ma daga bisa hanyar ta daina biyuwa.

An hangi fasinjoji da masu ababen hawa sun yi cirko-cirko a yayin da hanyar ta tsaya cak ba motsi.

Matafiyan dai, na fatan hukumomin lura da hanyoyi za su kai daukin gaggawa.

Hanyar dai ita ce babbar hanya da matafiya da suka fito daga Kano da Kaduna, Katsina da sauran su ke bi wajen zuwa babban birnin tarayya Abuja da kuma kudancin Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Tinubu ya Iso Kano domin ta’aziyyar Dantata

Shugaban Nigeria Bola Ahmad Tinubu ya iso jihar Kano...

ALGON ta Kano Sa’adatu Soja ta sami sabon matsayi a kungiyar ALGON ta Ƙasa

Daga: Aliyu Danbala Gwarzo. Shugabar karamar hukumar Tudunwada kuma ALGON...

Da dumi-dumi: Tinubu zai zo Kano

Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano ranar...

Tinubu ya sauya sunan jami’ar Maiduguri zuwa Sunan Muhd Buhari

Shugaba Bola Tinubu ya sauya sunan Jami'ar Maiduguri zuwa...