Alkalin alkalan Nigeria , Ariwoola ya yi ritaya

Date:

 

Babban mai shari’a na ƙasa na 22, Olukayode Ariwoola ya yi ritaya a matsayin Alkalan Alkalan Nijeriya bayan cika shekarun aiki na shekara 70.

Ariwoola, wanda aka haife shi a ranar 22 ga watan Agusta a 1954, ritayar tasa ta kawo karshen aikin da ya shafe shekaru yana yi a fannin shari’a.

A ranar 22 ga watan Nuwamba na 2011 ne aka nada mai shari’a Ariwoola a matsayin alkalin kotun koli , sannan ya sama babban mai shari’a na Nijeriya a 27 ga watan Yuni na 2022 bayan ajiye aikin da mai shari’a Tanko Muhammad yayi.

Tinubu ya yi wa Nigeria illar da za a dade ba a gyarata ba – Atiku Abubakar

A ranar 21 ga watan Satumba na 2022, majalisar dattawa ta tabbatar da shi a matsayin babban alkalin Nijeriya.

Anasa rai dai, Kudirat Kekere-Ekun ce za ta gaje shi bayan majalisar shari’a ta kasa NJC, ta bada shawarar nada ta a mukamin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...