Da dumi-dumi: Ogan Boye ya ajiye mukaminsa na Mai baiwa gwamnan Kano shawara Kan Matasa

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Amb. Imam Yusuf wanda aka fi sani da Oga Boye ya Ajiye mukaminsa na mai baiwa gwamnan jihar kano shawara kan harkokin matasa.

Ogan Boye ya Mika takardar ajiye aikin nasa ne a Ofishin Sakataren gwamnatin jihar kano a wannan rana ta talata.

Za a shafe kwana uku ana ruwa marka-marka a wasu jihohin Najeriya

Imam Yusuf ya ajiye mukaminsa nasa ne domin ya tsayawa takarar shugabancin Karamar Hukumar Nassarawa a cikin jam’iyyar NNPP Kwankwasiyya.

Idan za’a iya tunawa dokar Zaɓe ce ta ce dole duk mai sha’awar tsayawa takarar wata kujerar sai ya ajiye duk wani Mukami da aka nada shi kwana 90 kafin zaben.

Badakalar magungunan Kano: Mun fara bincike kuma za mu gurfanar da duk mai hannu – Muhuyi Magaji

Hakan nuni da cewa Ogan Boye ya shiga cikin jerin wadanda suke takarar shugabancin Karamar hukumar Nasarawa a zaɓen da za’a gudanar a ranar 30 ga watan Nuwanba mai zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...