Zanga-zanga: Bayan gurfanar da mutane 632, Gwamnan kano ya magantu kan masu daga tutar Rasha

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin jihar Kano ta sanar da gurfanar da wasu mutane 632 da ake zargi da lalata kayayyakin gwamnati da sace kayan jama’a da yayin da ake ci gaba da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a jihar.

Talla
Talla

Jaridar Kadaura24 ta ruwaito cewa, an ga matasa masu zanga-zanga, suna rera wakokin nuna adawa da gwamnati da kuma rike da tutar kasar Rasha, a wurare irin su Dakata, Rimin Kebbe, Gwammja, Zoo Road da dai sauransu.

Da yake jawabi a Kano, Kakakin Gwamnan Jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya bayyana cewa an kama wadanda ake tuhuma su 632 da laifin lalata dukiyar al’umma.

Zanga-zanga:APCn Kano ta mayar da zazzafan martani ga kalaman gwamna Abba Kabir

Dawakin Tofa ya yi gargadin cewa kudirin gwamnatin jihar Kano na wanzar da zaman lafiya ba abu ne da gwamnati zata yi wasa da shi ba, inda ya kara da cewa wadanda aka samu da laifin barna za su fuskanci doka.

Ya kara da cewa gwamnatin jihar na shirin samar da dimbin shirye-shiryen horas da matasa sana’o’i daban-daban domin inganta rayuwar su, domin dakile yiyuwar amfani da su wajen karya doka da oda.

Yanzu-yanzu: Tinubu ya dage taron FEC, ya karbi bakuncin shugabannin tsaro

Kakakin ya kuma sanar da cewa za a kafa kwamitin bincike na musamman da zai binciki wadanda ke da hannu wajen kashe-kashe da sace-sacen kayan jama’a a jihar.

Kwamitin zai tantance musabbabin kashe-kashe da lalata gine-ginen gwamnati, in ji shi.

Ya kara da cewa masu zanga-zangar da suke dauke da tutocin kasar Rasha ba su da alaka da gwamnati, don haka ya bukaci hukumomin tsaro da su bankado wadanda ke ingiza su da kuma manufarsu.

Ya bayyana cewa masu zanga-zangar na gaskiya a jihar sun mika kokensu da bukatunsu ga gwamnati, wanda ya ce za a mika su ga shugaba Bola Tinubu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...