Yanzu-yanzu: Tinubu ya dage taron FEC, ya karbi bakuncin shugabannin tsaro

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaba Bola Tinubu ya dage zaman majalisar zartarwa ta tarayya na wannan makon zuwa ranar da ba a bayyana ba, kuma a maimakon haka zai gana da shugabannin hukumomin tsaro na Nigeria.

Ana sa ran taron zai samu halartar mataimakin shugaban kasa, mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, da dukkan hafsoshin tsaro, da sufeto janar na ‘yan sanda, da kwanturola janar na kwastam, da na hukumar kula da shige da fice, da kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa.

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kaduna ta saka dokar hana fita

Majiyar da ke kusa da fadar shugaban kasa ta shaida wa gidan talabijin na Channels, cewa taron gaggawar da shugabannin tsaro ba zai rasa nasaba da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa da ake yi a fadin kasar ba.

Rahotanni sun nuna cewa ‘yan Najeriya wadanda galibi matasa ne su ke sake haduwa domin gudanar da zanga-zangar a a fadin kasar a rana ta biyar na zanga-zangar, inda wasu daga cikinsu ke dauke da tutocin ƙasar Rasha

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...