Yanzu-yanzu: Tinubu ya dage taron FEC, ya karbi bakuncin shugabannin tsaro

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Shugaba Bola Tinubu ya dage zaman majalisar zartarwa ta tarayya na wannan makon zuwa ranar da ba a bayyana ba, kuma a maimakon haka zai gana da shugabannin hukumomin tsaro na Nigeria.

Ana sa ran taron zai samu halartar mataimakin shugaban kasa, mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, da dukkan hafsoshin tsaro, da sufeto janar na ‘yan sanda, da kwanturola janar na kwastam, da na hukumar kula da shige da fice, da kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa.

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kaduna ta saka dokar hana fita

Majiyar da ke kusa da fadar shugaban kasa ta shaida wa gidan talabijin na Channels, cewa taron gaggawar da shugabannin tsaro ba zai rasa nasaba da zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa da ake yi a fadin kasar ba.

Rahotanni sun nuna cewa ‘yan Najeriya wadanda galibi matasa ne su ke sake haduwa domin gudanar da zanga-zangar a a fadin kasar a rana ta biyar na zanga-zangar, inda wasu daga cikinsu ke dauke da tutocin ƙasar Rasha

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...