Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta sassauta dokar hana fita

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar kano ta sanar da sassauta dokar hana fita ta awa 24 da ta sanya sakamakon yadda zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ta rikide zuwa tashin hankali.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa gwamnatin jihar kano ta sanya dokar ne tun a ranar Alhamis ranar farko kenan da fara Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa bayan wasu bata gari sun fake da zanga-zangar su ka rika fasawa da sace kayan gwamnati da na al’umma.

Duk da dokar hana fita, zanga-zanga ta dau sabon salo a Kano

” Daga gobe lahadi za a fara fita daga karfe 8 na safe zuwa karfe 2 na rana, har kuma aga abun da hali zai yi “.

Wannan na ƙunshe cikin wata sanarwa da kwamshinan yaɗa labarai na jihar Kano Baba Halilu Dantiye ya sanyawa hannu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...