Yanzu-yanzu: Gwamnatin Kano ta sassauta dokar hana fita

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Gwamnatin jihar kano ta sanar da sassauta dokar hana fita ta awa 24 da ta sanya sakamakon yadda zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa ta rikide zuwa tashin hankali.

Idan za a iya tunawa kadaura24 ta rawaito cewa gwamnatin jihar kano ta sanya dokar ne tun a ranar Alhamis ranar farko kenan da fara Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa bayan wasu bata gari sun fake da zanga-zangar su ka rika fasawa da sace kayan gwamnati da na al’umma.

Duk da dokar hana fita, zanga-zanga ta dau sabon salo a Kano

” Daga gobe lahadi za a fara fita daga karfe 8 na safe zuwa karfe 2 na rana, har kuma aga abun da hali zai yi “.

Wannan na ƙunshe cikin wata sanarwa da kwamshinan yaɗa labarai na jihar Kano Baba Halilu Dantiye ya sanyawa hannu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...