Yadda Aka Kama Lakcarorin Bogi A Jami’ar Bayero dake Kano

Date:

Wasu malaman jami’a na bogi sun shiga hannun jami’an tsaro a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).

Dubun malaman jami’ar na bogin ta cika ne a yayin da suke tsaka da sayar wa dalibai ’yan ajin farko da litattafan karatu.

Sanarwar da jami’ar ta fitar ɗauke da sa hannun Mukaddashin Magatakarda Jami’ar BUK Bala G. Abdullahi, ta ce lakcarorin bogin sun tursasa dalibai sayen litattafansu guda hudu a matsayin sharadin cin jarabawar darussan su.

Talla
Talla

Ya ce dubun mutanen biyu, Mista David Iluebe daga Jihar Edo da Mista Chike E. Eke daga Jihar Delta, ta cika ne bayan sun shiga dakin karatu a Tsangayar Karatun Injiniya, suka gabatar da kansu a matsayin lakcarori, suka tallata musu litattafai hudu.

Lakcarorin ba su tsaya nan ba, sun bayyana wa daliban cewa sayen litattafan wajibi ne kuma babu wanda zai ci jarabawa sai wanda ya saya.

Da dumi-dumi: Tinubu ya rage farashin Shinkafa a Nigeria

Magatakardan ya ce barazanar ta tilasta wa daliban sayen litattafan, amma daga bisani take-taken lakcarorin bogin ta sa jami’an tsaron jami’ar kama su.

Bayan samun korafi aka kama su, inda a halin yanzu ake tuhumar su da laifukan kutse, sojan gona, damfara da kuma cuta.

Ya ce lakcarorin bogin sun bayyana cewa karo na biyu ke nan da suka yi haka a Kano, domin a baya sun yi a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta jihar (Kano Poly).

Sun yi ikirarin wallafa littatafan da suke sayarwa kuma sun yi haka ne saboda rashin aiki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Amfani da al’ada a cikin fina-finan kannywood ne ya hana masa’antar ci gaba – Khadija Osi

Jaruma a masana'antar Kannywood Khadija Muhammad wacce aka fi...

Nasarar da Ɗaliban Kano suka Samu a NECO Kokari ne na Gwamnatin Ganduje – Sanusi Kiru

Tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Hon. Muhammad Sanusi...

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa...

Kano Ta Zama Zakara A Jarrabawa NECO Ta Bana

Hukumar shirya jarrabawar kammala sakandire ta Najeriya (NECO),ta fitar...