Zanga-zanga: IGP ya ba da sabon umarni ga DIGs, AIGs, CPs

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Sufeto Janar na ‘yan sanda (IGP), Kayode Egbetokun, ya umurci manyan jami’an ‘yan sanda da su kare wadanda suka shirya zanga-zangar da zanga-zangar tsadar rayuwa da aka yi mata take da #EndBadGovernance wadda aka shirya gudanarwa a ranakun 1 zuwa 10 ga Agusta, 2024.

Hakan na kunshe ne a cikin wasikar mayar da martani da babban sufeton ya aike wa lauyan nan mai kare hakkin dan Adam Ebun-Olu Adegboruwa.

Idan za a iya kadaura24 ta rawaito Adegboruwa, Babban Lauyan Najeriya (SAN), a ranar 26 ga Yuli, 2024, ya rubuta wa IGP wasikar neman a baiwa masu zanga-zangar kariya a yayin da zasu gudanar da ita.

Talla
Talla

Sufeto janar din, a cikin wasikar da mayar wa da lauyan martani mai dauke da kwanan wata 29 ga Yuli, 2024, ya umurci manyan jami’an ‘yan sanda da su saurari bukatar babban lauyan.

Tinubu ya dauki matakin da zai kawo karshen dambarwar Matatar Ɗangote da gwamnatin tarayya

Egbetokun ya mayar da martani ne a cikin wata wasika mai dauke da sa hannun babban jami’in ma’aikatan sa, CP Johnson Adenola.

Sufeto janar din ya kuma bukaci ganawa da Adegboruwa a Abuja a ranar Talata, 30 ga watan Yuli, 2024, domin a ci gaba da tattaunawa kan bukatarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...