Zanga-zanga: IGP ya ba da sabon umarni ga DIGs, AIGs, CPs

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

 

Sufeto Janar na ‘yan sanda (IGP), Kayode Egbetokun, ya umurci manyan jami’an ‘yan sanda da su kare wadanda suka shirya zanga-zangar da zanga-zangar tsadar rayuwa da aka yi mata take da #EndBadGovernance wadda aka shirya gudanarwa a ranakun 1 zuwa 10 ga Agusta, 2024.

Hakan na kunshe ne a cikin wasikar mayar da martani da babban sufeton ya aike wa lauyan nan mai kare hakkin dan Adam Ebun-Olu Adegboruwa.

Idan za a iya kadaura24 ta rawaito Adegboruwa, Babban Lauyan Najeriya (SAN), a ranar 26 ga Yuli, 2024, ya rubuta wa IGP wasikar neman a baiwa masu zanga-zangar kariya a yayin da zasu gudanar da ita.

Talla
Talla

Sufeto janar din, a cikin wasikar da mayar wa da lauyan martani mai dauke da kwanan wata 29 ga Yuli, 2024, ya umurci manyan jami’an ‘yan sanda da su saurari bukatar babban lauyan.

Tinubu ya dauki matakin da zai kawo karshen dambarwar Matatar Ɗangote da gwamnatin tarayya

Egbetokun ya mayar da martani ne a cikin wata wasika mai dauke da sa hannun babban jami’in ma’aikatan sa, CP Johnson Adenola.

Sufeto janar din ya kuma bukaci ganawa da Adegboruwa a Abuja a ranar Talata, 30 ga watan Yuli, 2024, domin a ci gaba da tattaunawa kan bukatarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...