Gwamnatin Nigeria ta fara yunkurin sassanta Ɗangote da hukumomin man fetur na kasar

Date:

Gwamnatin Najeriya ta fara yunƙurin sasanta rikicin saɓanin da aka samu tsakanin matatar mai ta Dangote da kuma hukumomin da ke kula da harkokin man a ƙasar.

Ƙaramin Ministan Man Fetur Heineken Lokpobiri ya ce ya jagoranci wani zama da Aliko Dangote shugaban kamfanin Dangote, da Mele Kyari shugaban kamfanin NNPCL, da Farouk Ahmed shugaban hukumar Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA), da Gbenga Komolafe shugaban Nigerian Upstream Petroleum Regulatory Commission (NUPRC) a yammacin yau Litinin.

Talla

“Ganawar wani yunƙuri ne na gano maganin matsalolin da matatar ke fuskanta,” in ji ministan cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

“Dukkan ɓangarorin sun nuna aniyarsu ta nemo bakin zaren kuma sun nuna jin daɗinsu da yunƙurin sasantawar da ake yi.”

Yadda Sarki Aminu da Yan Sanda suka kwace ni a hannu wasu matasa – Dan majalisar NNPP

Wannan ne karon farko da ɓangaren gwamnati ya yi magana kan cecekucen da ɓangarorin ke yi bayan hukumomin sun zargi matatar Dangote da fitar da man dizel maras inganci, wanda ta musanta ta hanyar gudanar da gwaji a gaba ‘yanmajalisar tarayya ranar Asabar.

Aliko ya koka kan yadda kamfanonin cikin gida suke ƙin sayar wa matatar tasa ɗanyen man fetur ɗin domin fara tace shi da kuma sayar da shi a Najeriya.

Rahotonni sun ce matatar ta mayar da hankali wajen sayo ɗanyen man daga ƙasashen Libya da Angola domin tace man da za ta fara fitarwa kasuwa a watan Agusta mai zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...