Gwamnatin Nigeria ta fara yunkurin sassanta Ɗangote da hukumomin man fetur na kasar

Date:

Gwamnatin Najeriya ta fara yunƙurin sasanta rikicin saɓanin da aka samu tsakanin matatar mai ta Dangote da kuma hukumomin da ke kula da harkokin man a ƙasar.

Ƙaramin Ministan Man Fetur Heineken Lokpobiri ya ce ya jagoranci wani zama da Aliko Dangote shugaban kamfanin Dangote, da Mele Kyari shugaban kamfanin NNPCL, da Farouk Ahmed shugaban hukumar Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA), da Gbenga Komolafe shugaban Nigerian Upstream Petroleum Regulatory Commission (NUPRC) a yammacin yau Litinin.

Talla

“Ganawar wani yunƙuri ne na gano maganin matsalolin da matatar ke fuskanta,” in ji ministan cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

“Dukkan ɓangarorin sun nuna aniyarsu ta nemo bakin zaren kuma sun nuna jin daɗinsu da yunƙurin sasantawar da ake yi.”

Yadda Sarki Aminu da Yan Sanda suka kwace ni a hannu wasu matasa – Dan majalisar NNPP

Wannan ne karon farko da ɓangaren gwamnati ya yi magana kan cecekucen da ɓangarorin ke yi bayan hukumomin sun zargi matatar Dangote da fitar da man dizel maras inganci, wanda ta musanta ta hanyar gudanar da gwaji a gaba ‘yanmajalisar tarayya ranar Asabar.

Aliko ya koka kan yadda kamfanonin cikin gida suke ƙin sayar wa matatar tasa ɗanyen man fetur ɗin domin fara tace shi da kuma sayar da shi a Najeriya.

Rahotonni sun ce matatar ta mayar da hankali wajen sayo ɗanyen man daga ƙasashen Libya da Angola domin tace man da za ta fara fitarwa kasuwa a watan Agusta mai zuwa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...