Sabbin Sarakunan Rano da Karaye sun ziyarci Sarki Sanusi II

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Sabbin sarakunan Rano da Karaye da aka nada a matsayin masu daraja ta biyu sun yi mubaya’a ga Sarkin Kano na 16 Malam Muhammadu Sanusi II a ranar Laraba.

Sun kai wa sarki Sanusi II ziyarar ne sa’o’i kadan bayan Gwamnan kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana nadin nasu.

Sabbin sarakunan sun hada da: Alhaji Muhammad Maharaz na Karaye, Muhammad Isah Umar na Rano, da Alhaji Aliyu Abdulkadir na Gaya.

Talla

A wani faifan bidiyo da wakilin kadaura24 ya gani, sarakunan masu daraja ta biyu sun yi mubaya’a ga Sarki Sanusi a zaman fadar da aka gudanar a ranar Laraba.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya soki gwamnatin Kano kan sabbin masarautu masu daraja ta biyu

Duk sarakunan biyu sun yi alkawarin yin aiki a karkashin masarautar Kano mai daraja ta daya tare da gode wa Gwamna Abba Yusuf bisa ganin sun cancanta har ya nada su .

Idan za a iya tunawa, a ranar jiya talata 16 ga Yuli, 2024, Gwamnan ya rattaba hannu a kan dokar kafa masarautu masu daraja ta biyu a jihar. Masarautar Rano da ta kunshi kananan hukumomin Rano, Kibiya, da Bunkure; sai masarautar Gaya da ta kunshi kananan hukumomin Gaya, Ajingi, da Albasu; ita kuma Karaye ta kunshi kananan hukumomin Karaye da Rogo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kamfanin Gerawa ya ba da tallafin Kwamfutoci 100 ga al’ummar Gezawa

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa   Kamfanin shinkafa na Gerawa Rice Mills...

Gwamnan Kano ya baiwa maja-baƙin Sheikh Karibullah da wasu malamai muƙami

    Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince...

Mamallakin jaridar Nigerian Tracker ya zama Ma’ajin kungiyar masu yada labarai a kafar yanar gizo ta Arewa

Kungiyar masu yada labarai a kafafen sadarwa na zamani...

Rusau: Ana zargin an harbi mutane 6 a unguwar Rimin zakara dake Kano

Daga Nazifi Dukawa   Mazauna Unguwar Rimin Zakara da ke Karamar...