Murtala Sule Garo ya taya Musulmin Nigeria Murnar Shiga Sabuwar Shekara

Date:

 

Tsohon dan takarar mataimakin gwamna a karkashin inuwar jam’iyyar APC a Jihar Kano, Alhaji Murtala Garo, ya taya al’ummar Musulmi murnar shigowa sabuwar shekarar musulunci ta 1446H.

Cikin wata sanarwa Alhaji Murtala Garo ya ce ya na fatan sabuwar shekarar za ta zama mai albarka ga al’ummar Musulmi a Jihar Kano da kasa baki daya.

Musa Iliyasu Kwankwaso ya kama aiki a mukamin da Tinubu ya bashi

“Ranar Lahadi ita ce daya ga watan sabuwar shekarar Musulunci ta 1446H kamar yadda Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya sanar.

Talla

“Ina taya al’ummar Musulmi na Jihar Kano da kasa baki daya murnar wannan rana mai albarka. Wannan rana ce mai matukar hamimmanci a duniyar Musulunci.
“Ina kira ga al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci dan habaka kaunar juna da jinkai tsakanin al’umma.

“Dukkan mu akwai rawar da za mu iya takawa dan gina al’umma da tabbatar da zaman lafiya kamar yanda addinin Musulunci ya koyar.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...