Daga Rukayya Abdullahi Maida
Kwamitin zaman lafiya na jihar kano ya yi kira ga al’ummar jihar da su guji shiga zanga-zangar yanayin tsadar rayuwa da ake ciki a kano kamar yadda wata majiya mai ƙarfi ta bayyana cewa ana shirin yin zanga-zangar.
Majiyar tace wasu muggan mutane sun shirya tsaf domin gudanar da zanga-zangar a jihar Kano.
Rikicin Masarauta: An Samu Tsaiko A Shari’ar Sarautar Kano
Shugaban sakatariyar kwamitin zaman lafiya na jihar Kano kuma shugaban kungiyoyin fararen hula na jihar Kano, Amb. Ibrahim Waiya ne ya bayyana hakan a wani saƙon murya da ya aikowa kadaura24.
Ya bayyana cewa jihar Kano ita ce jiha ɗaya tilo da arewacin najeriya ke alfahari da ita wajen samar da zaman lafiya, wanda hakan ne yasa jihar ta yi fice a harkokin kasuwanci na yau da kullum a ƙasa dama nahiyar Afirka gaba ɗaya .
Gwamnatin Kano ta tasamma warware rikicin ta da yan jaridun da sukai Mata tawaye
Amb. Ibrahim Waiya ya ce yanayin ƙuncin rayuwa da ake ciki kamata ya yi al’umma su koma ga Allah domin neman sauƙi kamar yadda aka duƙufa lokacin watan azumin Ramadana.
Waiya ya ƙara da cewa ya kamata al’umma su zama masu kishin jihar su domin ba su da jihar da ta fi ta a yanzu.