Hajjin bana: Yau wa’adin shigar Maniyata ƙasar saudiyya ke cika

Date:

Ranar Litinin din nan ce ranar da hukumomin ƙasar Saudiyya suka tsayar mastayin ranar cikar wa’adin kammala jigilar maniyyata aikin Hajjin bana daga kowace kusurwa ta duniya.

Da karfe 12 na tsakar daren yau Litinin agogon Saudiyya ne hukumomin na Saudiyya suka ce za su rufe filayen jiragen saman ƙasar 6 ga saukar duk wani jirgin da ya dauko maniyyata daga kowace kasa ta duniya.

Hakan ya sa ƙasashe musamman waɗan da ke da adadi mafi yawa na maniyyatan da ke rige-rigen ganin sun kammala jigilar maniyyatansu kafin cikar wa’adin.

Filayen jiragen su ne waɗan da aka keɓe domin jigilar maniyyatan na bana da ke biranen Riyadh, da Jiddah, da Madina, da Dammam, da Taif, da kuma Yanbu’u.

Kwankwaso ya bayyana wadanda suka hana gwamnan Kano sakat tsawon Shekara Daya

Sai dai hukumomin sun ce rufewar ba za ta shafi jiragen da suka ɗauko fasinjojin da za su shiga ƙasar domin kasuwanci, da yawon bude ido, da ziyaratar ƴan uwa da dukkan wata lalura da ba ta shafi aikin Hajji ba.

Yanzu haka dai ƙasashe duniya na ta fadin tashin ganin sun kammala jigilar maniyyatansu kafin cikar wannan wa’adin da hukumomin saudiyyan suka ɗibar musu.

Muhuyi Magaji ya fara bincike kan badakalar kudaden tallafin da gwamnan Kano ya baiwa matasa

Ranar Litinin din nan ce ranar da hukumomin ƙasar Saudiyya suka tsayar mastayin ranar cikar waadin kammala jigilar maniyyata aikin Hajjin bana daga kowace kusurwa ta duniya.

Da karfe 12 na tsakar daren yau Litinin agogon Saudiyya ne hukumomin na Saudiyya suka ce za su rufe filayen jiragen saman ƙasar 6 ga saukar duk wani jirgin da ya dauko maniyyata daga kowace kasa ta duniya.

Hakan ya sa ƙasashe musamman waɗan da ke da adadi mafi yawa na maniyyatan da ke rige-rigen ganin sun kammala jigilar maniyyatansu kafin cikar wa’adin.

Filayen jiragen su ne waɗan da aka keɓe domin jigilar maniyyatan na bana da ke biranen Riyadh, da Jiddah, da Madina, da Dammam, da Taif, da kuma Yanbu’u.

Sai dai hukumomin sun ce rufewar ba za ta shafi jiragen da suka ɗauko fasinjojin da za su shiga ƙasar domin kasuwanci, da yawon bude ido, da ziyaratar ƴan uwa da dukkan wata lalura da ba ta shafi aikin Hajji ba.

Yanzu haka dai ƙasashe duniya na ta fadin tashin ganin sun kammala jigilar maniyyatansu kafin cikar wannan wa’adin da hukumomin saudiyyan suka ɗibar musu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...