Kungiyar Northern Reform Organization ta bukaci wakilan Arewa a majalisar zartarwar ta kasa da majalisar kasa da su himmatu don ganin gwamnatin tarayya ta kammala aiyukan da ba ta kammala ba a yankin.
“Akwai muhimman aiyuka da ya kamata gwamnatin tarayya ta kammala su, wadanda zasu taimaka sosai wajen ciyar da yankin Arewacin Nigeria gaba”.
Fargaba a Kano: Sarki Sanusi da Sarki Aminu na shirin gabatar da Sallar Juma’a a Masallacin Guda
Kungiyar ta bayyana hakan ne a cikin wani sakon taya murnar cika shekara da hawa mulkin ga shugaban kasa Bola Tinubu da daraktan yada labaran kungiyar Mahmoud Adnan Audi ya sanyawa hannu kuma ya turowa kadaura24.
Sanarwar ta ce akwai aiyuka da suka hadar da aikin kamfanin sarrafa karafa na Ajaokuta da aikin yashe Kogin River Niger da aikin hakar danyan man da aka samo a kolmani a iyakar Bauchi – Gombe da dai sauransu.
Yan Sanda sun magantu kan shirin Sarki Aminu da Sarki Sanusi na yin sallar juma’a a masallaci guda
Sanarwar ta kuma bukaci gwamnatin tarayya da ya mai da hankali wajen kammala aikin titin kano zuwa Abuja da kuma na Kano zuwa Katsina da na Legos zuwa illori zuwa kaduna da sauran su.
Sanarwar ta kuma kara da cewa ya kamata gwamnatin tarayya ta yi duk mai yiwuwa don ganin ta magance matsalolin tsaro da suka addabi wasu daga cikin jihohin Arewacin Nigeria.
Ta kuma taya shugaban ƙasa Bola Tinubu murnar cika shekara daya akan karagar mulkin Nigeria.