Wata Kotun a kano ta bada umarni akan yar siyasar nan Sadiya Dauda Ican Kabari

Date:

Daga Ibrahim Aminu Riminkebe.

 

Babbar kotun shari’ar musulunci dake zaman ta a shahuci karkashin jgaorancin mai shari’a Malam Abdu Abdullahi Wayya, ta bada umarnin ayo sammacin ‘yar siyasar nan mai suna Sadiya Dauda Ican Kabari ta ko wacce ta hanya.

A zaman kotun na yau laraba, lauyan bangaran masu kara Barista Tanimu ya bayyana wa kotun cewa wacce ake zargin ta jima tana gujewa shari’a, duk da sammacin da kotun tayi umarnin a baiwa Sadiya Dauda Ican Kabari domin ta bayyana a gaban kotun.

Barista Tanimu ya shaidawa kotun cewa, wacce ake zargin ta yi wani fefan bidiyo Inda ta bata sunan mahaifi mai kara Adamu Abdullahi Karkasara wanda kuma ta watsa bidiyo a kafafan sada zumunta.

Abun da ya faru a majalisar dokokin jihar kano kan batun gyaran dokar masarautu

Hakazalika lauyan masu kara ya sake bayyanawa kotun cewa, mako guda kenan ana neman Sadiya Ican Kabari domin a bata sammacin amma tana kaucewa hakan saboda yadda ta rufe daukacin wayoyin da take amfani dasu.

Hajjin Bana: Ƙasar Saudiyya Ta Samar Da Wata Lema Ta Musamman Ga Mahajjata

Daga bisani mai shari’a Malam Abdu Abdullahi Wayya, ya amince da rokon bangaran masu kara suka yi, tare da yin umarnin sake aikewa Sadiya Dauda Ican Kabari sabon sammacin ta hanyar like mata shi a kofar gidan ta da sakon tartakwana da kuma hanyar Whatsapp domin ta bayyana a kotun.

 

Alkalin kotun ya dage sauraron shari’ar zuwa ranar biyar ga watan gobe domin ci gaba da sauraron shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...

Budaddiyar Wasika ga Gwamnan Kano kan wanda zai maye gurbin Muhuyi Magaji R/gado daga Kungiyar Lauyoyi yan Kano

Zuwa ga Mai Girma Alhaji Abba Kabir Yusuf Gwamnan Jihar Kano Gidan...

Dan majalisa Bichi ya sake biyan kuɗin makarantar dalibai 121 masu karatun digiri na biyu da na digirin digirgir

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi a Majalisar...