Wata Kotun a kano ta bada umarni akan yar siyasar nan Sadiya Dauda Ican Kabari

Date:

Daga Ibrahim Aminu Riminkebe.

 

Babbar kotun shari’ar musulunci dake zaman ta a shahuci karkashin jgaorancin mai shari’a Malam Abdu Abdullahi Wayya, ta bada umarnin ayo sammacin ‘yar siyasar nan mai suna Sadiya Dauda Ican Kabari ta ko wacce ta hanya.

A zaman kotun na yau laraba, lauyan bangaran masu kara Barista Tanimu ya bayyana wa kotun cewa wacce ake zargin ta jima tana gujewa shari’a, duk da sammacin da kotun tayi umarnin a baiwa Sadiya Dauda Ican Kabari domin ta bayyana a gaban kotun.

Barista Tanimu ya shaidawa kotun cewa, wacce ake zargin ta yi wani fefan bidiyo Inda ta bata sunan mahaifi mai kara Adamu Abdullahi Karkasara wanda kuma ta watsa bidiyo a kafafan sada zumunta.

Abun da ya faru a majalisar dokokin jihar kano kan batun gyaran dokar masarautu

Hakazalika lauyan masu kara ya sake bayyanawa kotun cewa, mako guda kenan ana neman Sadiya Ican Kabari domin a bata sammacin amma tana kaucewa hakan saboda yadda ta rufe daukacin wayoyin da take amfani dasu.

Hajjin Bana: Ƙasar Saudiyya Ta Samar Da Wata Lema Ta Musamman Ga Mahajjata

Daga bisani mai shari’a Malam Abdu Abdullahi Wayya, ya amince da rokon bangaran masu kara suka yi, tare da yin umarnin sake aikewa Sadiya Dauda Ican Kabari sabon sammacin ta hanyar like mata shi a kofar gidan ta da sakon tartakwana da kuma hanyar Whatsapp domin ta bayyana a kotun.

 

Alkalin kotun ya dage sauraron shari’ar zuwa ranar biyar ga watan gobe domin ci gaba da sauraron shari’ar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Zargin Almundahana: ICPC zata gurfanar da shugaban hukumar zabe ta Kano da wasu mutum biyu

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta (ICPC)...

Dalilin da ya hana ni zuwa Kano tarbar Tinubu – Ganduje

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Tsohon shugaban jam’iyyar APC na kasa,...

Shugaban RATTAWU na Kano ya taya sabbin shugabannin kungiyar na kasa murna

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Shugaban kungiyar ma’aikatan rediyo, Talabijin da...

Dalilina na ziyartar gwamnan Kano Abba – Inuwa Waya

Daga Rahama Umar Kwaru Tsohon Wanda ya nemi Zama Dan...