Abubunwan da ake tsammani zasu faru a majalisar dokokin Kano Kan dokar masarautu

Date:

Bayanan da ke fitowa daga majalisar dokokin jihar Kano na cewa a yau ne ‘yan majalisar za su kammala aiki a kan dokar da ta kafa sabbin masarautu a jihar.

Waɗansu majiyoyi masu ƙarfi sun tabbatar wa BBC cewa ‘yan majalisar za su soke dokar da aka yi a shekarar 2019, wadda ta bayar da damar kafa ƙarin manyan masarautu huɗu a cikin jihar.

Abun da ya faru a majalisar dokokin jihar kano kan batun gyaran dokar masarautu

Dokar ta ƙirkiri masarautar Bichi da ta Karaye da ta Gaya da kuma masarautar Rano.Tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ne ya sanya hannu a dokar a watan Disambar 2019.

A halin yanzu dai an girke jami‘an tsaro a wurare da dama na birnin Kano domin kauce wa tashin hankali.

Waɗansu majiyoyi a Kano ɗin sun tabbatar da cewa da zarar majalisar ta kammala kwaskwarima a kan dokar, ba tare da ɓata lokaci ba za ta mika wa gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf .

Kuma ana sa ran gwamnan na Kano zai sanya hannu a kan dokar kafin sanar da rushe sabbin masarautun da aka kafa a shekara ta 2019.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rasuwar Buhari: Majalisar Nigeria ta dakatar da duk aiyukanta

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Majalisar dokokin Nigeria ta dage zamanta...

Gwamnati ta baiwa ma’aikata hutu saboda rasuwar Muhammad Buhari

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gwamnatin jihar Katsina karkashin gwamna Umar...

Bayan tura Kashim ya taho da gawar Buhari, Tinubu ya ba da umarnin sassauta Tutar Nigeria

Shugaban kasa Bola Tinubu ya bada umarnin ayi kasa...

Yanzu:yanzu: Tsohon shugaban Nigeria Buhari ya rasu

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un!!! Allah yayi wa tsohon shugaban...