Mata 100 sun amfana da tallafin Naira dubu 50 – 50 a karamar hukumar Tudun wada

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Kantoman karamar hukumar Tudun wada a jihar kano Dr. Umar Isah Rugu-Rugu ya jagoranci raban tallafin kudi naira dubu hamsin ga mata 100 domin su ja jari su dogara da kawunan su .

Da yake jawabi yayin tallafin Dr. Umar isah rugu-rugu ya yabawa gwamnatin jihar kano karkashin jagorancin mai girma gwamna Alh. Abba kabir yusuf bisa yadda ta ke kokarin raba irin wannan tallafin ga Al’umma duba da halin matsin rayuwa da Al’umma suka tsinci kansu ciki.

Hasashen yanayin da zai kasance yau Asabar a birnin Kano da wasu jihohin Nigeria

Dr. Umar isah rugu rugu yakara da cewa ” An baku wannan jali ba dan komai ba sai domin aje a cigaba da gudanar da sanao’i wadanda basa sana’ar kuma su nemi sana’o’in da za su yi domin kowa ya samu kuma ya dogaro da kansa.

Kantoman Karamar hukumar Bichi ya ba da umarni ga wadanda aka baiwa filaye a yankin

“Muna fatan za kuyi dukkanin mai yiwuwa wajen amfanar da kanku da sauran al’umma kuma Muna fata wannan tallafin zai zamo silar arzin ku”.

Rugu-rugu yaja hankalin al’ummar yakin musamman wadanda basu samu a wannan karon ba da su yi hakuri wannan shi ne karon farko kuma za’a cigaba da bayar da irin wadannan tsare tsaren a nan gaba .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...

Bai dace ɗalibai su rika murnar kammala karatu ta hanyoyin da ba su dace ba – Mal Ibrahim Khalil

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa ‎ ‎ ‎Shugaban majalisar Malamai ta jihar Kano...